in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana gwabza fada a yankin yammacin Yemen
2017-01-23 10:52:47 cri
Rahotanni daga rundunar sojin kawance na cewa, cikin sa'o'i 24 da suka gabata, dakarun kawance da Saudiyya ke jagoranta, sun kai hari kan 'yan tawayen Houthi, inda suka kwace iko da yankunan gabar ruwa na yammacin, da kuma na gabar tekun Mocha dake Yemen.

Wani jami'in rundunar sojin ta hudu, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, dakarun dake goyon bayan gwamnati, sun tunkari gabar ruwa ta Mocha, inda suka kwace iko da sassan dake yankin, bayan wani kazamin fada.

Jami'in wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce kawo yanzu, ana ta gwabza fada a yankin, kuma dakarun za su ci gaba da tunkarar tekun Mocha.

Majiyoyi daga jami'an kiwon lafiya na cewa, sama da mayakan Houthi hamsin da sojojin kawance goma sha tara ne suka rasa rayakansu yayin fadan.

Jiragen yakin rundunar kawance da Saudiyya ke jagoranta sun taka muhimmiyar rawa wajen taimakawa sojojin kwace yankunan gaabar ruwan yammacin Yemen da kuma hanyar ruwa ta Bab Al Mandab. ( Fa'iza Mustapha )

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China