in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin gwamnatin Libya sun kwace yankin yammacin kasar
2017-11-09 09:22:58 cri
Rahotanni daga kasar Libya na cewa, sojojin gwamnatin Libya dake samun goyon bayan MDD sun yi nasarar kwace baki dayan yankin Warshaffana dake yammacin kasar, 'yan sa'o'i bayan kwace babban sansanin sojin dake yankin.

Wata majiyar soja ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, an shafe sama da mako guda ana gwabza fada tsakanin kungiyoyin 'yan tawaye masu dauke da makamai dake gaba da juna da sojojin gwamnati, a wani mataki na kakkabe munanan laifuffuka a yankin, lamarin da ya kai ga kisa tare da jikkata mayakan da yawansu ya kai 40, yayin da sojojin gwamnati 4 suka mutu kana wasu 10 kuma suka ji rauni.

Majiyar ta kara da cewa, tun a ranar Larabar da ta gabata ce, sojojin gwamnati suka kwace sansanin soja mafi girma dake yankin Warshaffana.

Ofishin hulda da jama'a na sojojin ya sanar da cewa, kwamandan sojojin dake gabashin kasar, janar Khalifa Haftar, ya gana da kwamandojin soja dake yankin na Warshaffana, jim kadan bayan da sojojin gwamnatin suka sanar da kwace iko da yankin baki daya. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China