in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a sake bude ofishin Jakadancin Birtaniya a Libya
2017-11-03 10:55:11 cri
Jakadan Birtaniya a Libya Peter Millet ya ce ofishin Jakadancin kasarsa na shirye-shiryen komawa aiki a Tripoli babban birnin kasar Libya.

Peter Millet ya sanar da haka ne a jiya, lokacin da yake ganawa da Fayez Serraj, firaministan gwamnatin Libya da MDD ke marawa baya.

A cewar ofishin yada labarai na Firaministan, Peter Millet ya ce nan bada dadewa ba, za a bude ofishin jakadancin Birtaniya a Tripoli, shekaru 3 bayan rufe shi bisa tabarbarewar tsaro a kasar.

Jami'an biyu sun kuma tattauna kan hadin giwar dake tsakani Birtaniya da Libya, tare da yanayin da tsaron Libya ke ciki a baya-bayan nan.

Fayez Serraj ya kuma sabunta kira ga kasashen duniya su gaggauta gudanar da cikakken bincike kan hari ta sama da wani jirgin da ba a san inda ya fito ba, ya kai birnin Derna dake gabashin kasar a kwanakin baya, al'amarin da ya yi sanadin gomman rayuka, ciki har da fararen hula. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China