in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun sojin Libya sun dakile yunkurin fasa-kwaurin makamai zuwa Sudan
2017-10-26 10:16:58 cri
Kafafen yada labaran cikin gidan Libya sun bayyana cewa dakarun sojin kasar sun yi nasarar dakile wani yunkurin fasa-kwaurin makamai zuwa makwabciyar kasar wato Sudan.

Abdarrahman Al-Kilani, kwamandan rundunar sojin Libya mai suna Subul Assalam mai alaka da dakarun soji dake gabashin kasar, yace bataliyar sojin ta kakkabe yunkurin fasa-kwaurin makamai da alburusai ne wanda aka yi niyyar shigar da su Sudan bayan da mazauna birnin kudancin Kufra suka yi korafin cewa wasu 'yan tada kayar baya na kasar Sudan sun kulla wata yarjejeniyar cinikin makamai da alburusai da suke son shigowa da su cikin kasar.

Al-Kilani ya ce, tuni bataliyar sojin ta tura dakarunta don yin barin wuta a wani waje mai nisan kilomita 300 dake birnin kudancin kasar, kuma sun yi nasarar cafke tsagerun tare kuma da kwace dukkan makaman da kuma alburusan.

A watan Yuni ne bataliyar Subul Assalam ta amsa kiran da babban kwamandan rundunar dake gabashi janar Khalifa Haftar ya yi, inda ya bukaci a rufe kan iyakokin kasashen Libya da Chadi da Sudan, kuma ya bada umarnin a kama duk wata mota dake zirga-zirga a tsakanin iyakokin kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China