in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta nemi a gudanar da bincike game da kisan gilla a Libya
2017-10-30 10:11:08 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya na MDD a kasar Libya (UNSMIL), ya bukaci a gaggauta bincike game da kashe mutane 36 da aka yi a birnin Benghazi da ke gabashin kasar Libya.

A wani sakon da ya fitar ta shafukan sada zumunta na zamani,"UNSMIL, ta nemi a gaggauta binciko wadanda keda hannu wajen aikata kisan don gurfanar dasu a gaba shari'a.

UNSMIL ta yi Allah wadai da babbar murya game da aikata wannan mummunan laifi na kisan mutane 36 wadan da aka tsinci gawarwakinsu a yankin Abyar.

Rundunar soji dake da sansaninta a gabashin kasar ce ta bada umarni a ranar Asabar, inda ta nemi a gaggauta bincike game da faruwar lamarin.

Wata majiya daga sojoji ta bayyana cewa, mazauna garin Abyar, wanda keda tazarar kilomita 50 a kudu maso yammacin Benghazi, sun bada rahoton cewa an gano gawarwakin mutanen 36 da aka hallaka wadanda aka ga raunukan harbin bindiga a jikinsu a wani lungu a yankin.

A watan Yulin shekarar 2016 ma, jami'an tsaro sun tsinci gawarwakin wasu mutanen 14 da daure da ankwa a hannayensu a kusa da helkwatar Benghazi.

A watan Oktoban 2016, an tsinci gawarwakin mutane 10 wadanda aka hallaka su da harbin bindiga a gidan yarin soji na Benghazi.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China