in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin MDD ya yaba da kafa kwamitin hadaka a Libya
2017-10-25 09:08:53 cri
Shugaban shirin wanzar da zaman lafiya na MDD a Libya Ghassan Salame, ya ce ya ji dadi da aka kafa kwamitin hadaka dake wakiltar majalisar wakilan Libya, da majalisar koli ta kasar.

Ghassan Salame ya bayyana haka ne lokacin da yake ganawa da manema labarai jiya Talata, bayan ya gana da ministan harkokin wajen kasar Mohammed Sayala a Tripoli, babban birnin Libya.

A ranar Asabar da ta gabata ne aka kammala zagaye na biyu, na tattauna yarjejeniyar yi wa tsarin siyasar kasar garambawul a kasar Tunisiya, wanda shirin wanzar da zaman lafiya na MDD dake Libyan ya dauki nauyi.

A tsakiyar watan Satumba ne Ghassan Salame, ya gabatar da wani kuduri dake da nufin kawo karshen rikicin siyasa a kasar. Kudurin ya kunshi yi wa yarjejeniyar ta yanzu da MDD ke marawa baya garambawul da gudanar da babban taron kasa karkashin jagorancin MDD, wanda dukkan bangarorin siyasar kasar za su halarta da kuma zaben shugaban kasa da mambobin majalisar dokoki. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China