in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta dauki matakai game da masu satar fasaha da yin jebun kayayyaki
2017-11-07 09:02:29 cri
Mataimakin firaministan kasar Sin Wany Yang ya bayyana cewa, wajibi ne mahukuntan kasar su kara daukar kwararan matakai game da masu satar mallakar fasaha da yin jebun kayayyaki.

Wanga wanda mamba ne a zaunannen kwamitin hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, ya ce muddin ana bukatar a biya bukatun jama'a na samun rayuwa mai inganci a sabon zamanin da ake ciki da kuma kasa mai hankoron kirkire-kirkire, wabiji ne a kawar da wadannan matsaloli.

Jami'in na kasar Sin wanda ya bayyana hakan yayin taro na 12 na kungiyar yaki da masu satar mallakar fasaha da yin jebun kayayyaki ta kasa, ya ce ko da yake ba a kai ga magance wadannan matsaloli baki daya ba, amma yanzu haka yanayin kasuwa da matakan kare muradun masana'antu da masu sayayya sun inganta, biyo bayan nasarar da aka samu wajen magance wadannan matsaloli, kuma nan ba da dadewa ba za su zama tarihi.

Wang ya ce kasar Sin za ta ci gaba da daukar matakan ganin an magance matsalar masu satar mallakar fasaha da jebun kayayyaki da ake fitarwa zuwa kasashen dake kan hanyar ziri daya da hanya daya, ta yadda za a kare martabar kayayyaki kirar kasar Sin. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China