in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane kimanin 40 sun mutu a sakamakon harin bom da aka kai a gabashin kasar Syria
2017-11-06 10:52:09 cri
Gidan rediyon Sham FM na kasar Syria ya sanar a jiya cewa, harin da aka kai ta hanyar dana bam cikin wata mota a birnin Deir ez-Zor dake gabashin kasar Syria a ranar Asabar ya haddasa mutuwar fararen hula kimanin 40 tare da raunata mutane da dama.

Rahotanni na cewa, an kai harin ne a wata tashar binciken ababan hawa dake arewacin birnin Deir ez-Zor, wadda karkashin ikon sojojin Syria dake karkashin jagorancin dakarun yankin Kurdawa.

Kamfanin dillancin labaru na kasar Syria ya bayar da labari cewa, an kai wani harin bam a sansanin 'yan gudun hijira, inda maharin ya kutsa da mota shake da bama-bamai cikin sansanin 'yan gudun hijirar, harin ya kuma haddasa mutuwa da raunatar mutane da dama ciki har da mata da yara.

Kungiyar dake binciken batun kare hakkin dan Adam ta kasar Syria mai cibiya a birnin London na kasar Birtaniya ta bayyana cewa, kungiyar IS ce ta kai wannan hari.

A jiya ne, sojojin gwamnatin kasar Syria suka shiga birnin Deir ez-Zor, inda suka kwace birnin daga hannun mayakan IS, bayan da suka shafe shekaru 3 suna rike da birnin. Bangaren soja na kasar Syria ya sanar a ranar 3 ga wannan wata cewa, yanzu birnin Deir ez-Zor ya fita daga hannun kungiyar IS. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China