in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saudiyya ta dakile harin makami mai linzami da 'yan tawayen Houthi na Yemen suka kai mata
2017-11-05 13:33:32 cri
Rahotanni daga gidan talabijin na kasar Saudiyya sun ce, dakarun Saudiyya sun dakile wani harin makami mai linzami wanda 'yan tawayen Houthi dake kasar Yemen suka kaiwa filin jirgin saman birnin Riyadh, sai dai lamarin bai haddasa hasarar rayuka ko dukiya ba.

Rahotannin sun ce, wannan shi ne karon farko da 'yan tawayen Houthi suka kai harin makami mai linzami kan fadar mulkin kasar Saudiyya wato Riyadh, tun bayan da Saudiyya da wasu kasashe suka fara fatattakar 'yan tawayen shekaru biyu da suka shude.

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Saudiyya ta fitar da wata sanarwa dake cewa, a halin yanzu filin jirgin saman birnin Riyadh na ci gaba da ayyukanta yadda ya kamata, babu wata matsala game da tashi ko saukar jiragen sama a filin jirgin.

Jiya Asabar da dare, an jiyo babbar karar fashewar wani abu a birnin Riyadh, mai tazarar kilomita 45 da filin jirgin saman birnin, yayin da dakarun kasar suka dakile harin daga kasar Yemen.

Tun a ranar 1 ga watan da muke ciki, dakarun hadin-gwiwar kasashe daban-daban dake karkashin jagorancin Saudiyya sun yi luguden wuta kan wani wuri dake arewacin kasar Yemen, inda 'yan tawayen Houthi suka ce, dakarun suka kai hari kan wani otel, lamarin da yayi sanadiyyar hallaka fararen-hula 26. Amma a cewar bangaren Saudiyya, dakarun sun kai hari ne kan wata matattarar 'yan tawayen Houthi, lamarin da ya yi ajalin mayakan da dama, ciki har da kwararru a fannin sarrafa makamai masu linzami.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China