in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Saudi ta damke mayakan IS 46 bisa zarginsu da hannu a harin ta'addanci
2017-05-01 12:24:53 cri
Ratotanni daga kafar yada labarai ta Al Arabiya na cewa, ma'aikatar cikin gidan Saudiyya ta sanar a jiya Lahadi cewa, ta damke mayakan kungiyar IS mai da'awar kafa daular Musulunci su 46 wadanda take zarginsu da hannu wajen shirya harin kunar bakin wake a masallacin manzon Allah S.A.W dake birnin Madina a shekarar.

A cewar mai magana da yawun ma'aikatar cikin gidan kasar, wadanda ake zargin sun hada da 'yan asalin kasar Saudiyyan 32, da 'yan kasashen waje 14 da suka hada da kasashen Pakistan, Yemen, Afghanistan, Masar, Jordan da kasar Sudan, kuma tuni aka tsare mutanen a yammacin birnin Jeddah.

Jami'in ya ce ana zargin mutanen da hannu wajen kitsa harin ta'addanci wanda aka kaddamar kan masu ibada a masallacin manzon Allah S.A.W a shekarar data gabata.

Ya kara da cewa, ana zargin mutanen da kaddamar da harin ta'addanci a wani yanki na asibitin Suleiman Fakih dake Jeddah a shekarar bara.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China