in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Saudiyya ta ce ba ta tuntubi kasar Iran kan harkokin diflomasiyya ba
2017-09-06 14:50:14 cri
A jiya Talata, ministan harkokin wajen kasar Saudiyya Adel al-Jubeir wanda ke ziyarar aiki a kasar Burtaniya, ya musunta yiyuwar kulla wata mu'amalar diflomasiyya da kasar Iran.

A yayin wani taron manema labaru da ya gudana a jiya, a ofishin jakadancin kasar Saudiyya dake Burtaniya, Adel al-Jubeir ya ce, bangarorin Saudiyya da Iran, ba su yi wata mu'amala da ta shafi siyasa ba in ban da harkar ibada ta aikin hajji.

Don haka ya zuwa wannan lokaci ba batun kome ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Adel al-Jubeir ya kara da cewa, idan kasar Iran tana son kyautata dangantakar dake tsakaninta da Saudiyya, to ya zama wajibi ta yi gyaran fuska ga manufofinta na diflomasiyya, ta kuma dakatar da nuna goyon baya ga ta'addanci, kana ta daina tsoma baki kan harkokin cikin gidan sauran kasashe, ta kuma rika girmama dokokin kasa da kasa. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China