in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tanzaniya na sa ran kara jawo karin masu yawon bude ido daga kasar Sin
2017-11-04 12:32:14 cri
Shugaban hukumar kula da harkokin yawon bude ido na kasar Tanzaniya Thomas Mihayo, ya bayyana cewa, kasarsa na sa ran kara jawo karin masu yawon bude ido daga kasar Sin.

Yayin wani dandalin tattaunawa kan raya sana'ar yawon bude ido wanda aka yi jiya Jumma'a a birnin Dar es Salaam, Mihayo ya ce, sana'ar yawon shakatawa na daya daga cikin muhimman sana'o'in Tanzaniya. Yayin da layin dogo da ya hada Tanzaniya da Zambiya ke taimakawa ci gaban sana'ar yawon bude ido a Tanzaniya, ana fatan kara samun Sinawa da za su je yawon shakatawa kasar. Mihayo ya kuma yi imanin cewa, irin kyakkyawan muhallin namun daji gami da wuraren shakatawa na bakin teku dake Tanzaniya, za su burge Sinawa.

Shi ma a nata bangaren, jakadar kasar Sin dake Tanzaniya, Wang Ke ta yi imanin cewa, sakamakon kokarin da Sin da Tanzaniya suka yi, na kara tallata wuraren yawon shakatawa na Tanzaniya, tana mai cewa za'a kara samun masu yawon shakatawa daga kasar Sin. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China