Gabanin tsige Mramba, shugaba Magufuli ya shaidawa taron mabiya addinin kirista a wata majami'a da ke yankin Kagera cewa, karin kudin wutan da hukumar ta yi zai kawo koma baya ga shirin da kasar take yi na farfado da masana'antunta.
Wata sanarwar da sashen watsa labarai na fadar shugaban kasar ya rabawa manema labarai ta bayyana cewa, shugaba Magufuli ya nada Tito Mwinuka domin maye gurbin Mramba a matsayin manajan darektan hukumar. (Ibrahim Yaya)