in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tanzaniya ta musanta sa hannu cikin harkokin zaben Kenya
2017-07-25 10:26:25 cri

Tanzaniya ta sake musanta ta sa hannu cikin harkokin zaben kasar Kenya wanda za a gudanar a ranar 8 ga watan Augusta mai zuwa.

Ministar harkokin wajen kasar Augustine Mahiga, ta ce rahotanni da wasu kafafen yada labarai na Kenya suka ruwaito dake cewa Tanzania tana shiga harkokin zaben kasarsu, ba su da tushe bare makama.

Yayin wani taron manema labarai da aka yi a Dar es Salaam, babban birnin hada-hadar kasuwanci ta kasar, Augustine Mahiga, ta ce Tanzaniya ba ta taba ba, kuma ba za ta sa hannu cikin harkokin zaben kasashen waje ba, ciki kuwa, har da zaben kasar Kenya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China