in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta kaddamar da horar da sabbin 'yan sandan da aka tura Somalia
2017-10-08 12:40:17 cri
Shirin wanzar da zaman lafiya na Tarayyar Afrika dake aiki a Somalia AMISOM, ya kaddamar da wani horar da 'yan sandan wanzar da zaman lafiya 39, domin su kara fahimtar manufofin shirin da ka'idojin aiki.

Wata sanarwa da shirin ya fitar a jiya Asabar, ta ce 'yan sandan da suka fito daga Kenya da Uganda da Zambia da Nijeriya za su kasance a Somalia tsawon shekara guda suna rangadin aiki, inda za su horar da takwarorinsu na Somalia yadda za su yi hulda da al'umma wajen tabbatar da tsaro.

Da yake kaddamar da horon, kwamishinan 'yan sandan shirin AMISOM Brig-Janar Anand Pillay, ya shaidawa jami'an cewa, shirin na da ka'idojin aiki kuma zai ba kowanne daga cikin su kwafinsa, domin su fahimci abun da ake bukata daga gare su ta fuskar ladabi da biyayya da yanayin aiki da kuma yadda za su yi hulda a tsakaninsu da kuma al'ummar Somalia.

Horon zai shafi wasu maudu'i da suka hada da kare cin zarafin mata yayin rikici da kare yara da bada agajin jin kai da tsaron al'umma da kuma kare hakkokin bil'adama da tsarin al'adu.

Kwamishinan ya kuma bukaci jami'an su kasance masu ladabi da biyayya a ko da yaushe tare da yin aiki tukuru domin ba da gudunmuwa wajen farfado da Somalia. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China