in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar cudanya da kasashen waje ta Sin ta yi bayani ga jakadun kasashen waje game da tunanin babban taron JKS karo na 19
2017-11-01 15:35:33 cri
A yau ranar 1 ga wata, ma'aikatar harkokin cudanya da kasashen waje ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta Sin, ta gudanar da wani taro na musamman, inda ta yi bayani ga jami'an diplomasiyya da kungiyoyin ciniki, da wakilan kamfanoni na kasashen waje game da tunanin babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 19.

Jami'an diplomasiyya daga kasashe fiye da 150 guda fiye da 260 ciki har da jakadun kasashen waje dake kasar Sin ko mukaddashin jakadun fiye da 90 sun halarci taron.

Jami'an sun bayyana cewa, babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 19 yana da babbar ma'ana, inda aka gabatar da tunanin shugaba Xi Jinping game da tsarin mulki na gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin a sabon zamani da ake ciki, tare da wasu manyan matakan da suka dace da yanayin kasar Sin, wadanda suke nufin makomar bunkasuwar kasar ta Sin, tare da yin babban tasiri ga samun zaman lafiya da wadata da bunkasuwa a duniya gaba daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China