in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen raya tattalin arziki, in ji ministan harkokin wajen Libya
2017-10-29 13:30:11 cri
Ministan harkokin wajen gwamnatin hadin gwiwar jama'a ta kasar Libya Mohamed Sayala, ya bayyana cewa, kasar Sin ta taka mihimmiyar rawa wajen raya tattalin arziki, sakamakon tsarin yin kwaskwarima da bude kofa ga kasashen waje da ta aiwatar karkashin jagorancin Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin.

Mr. Sayala ya ce, kasar Sin dake karkashin jagorancin JKS, ta cimma nasara wajen neman bunkasuwar kasa baki daya. Kuma tattalin arziki kasar Sin ya ci gaba da bunkasa cikin sauri, lamarin da ya sa, kasar ta kasance kasa ta biyu wajen samun saurin bunkasuwar tattalin arziki a nan duniya. Wannan shi ne babbar nasara da kasar ta cimma.

Haka kuma ya nuna cewa, kasar Sin tana maida hankali kan neman daidaito a tsakanin bunkasuwar zamantakewar al'umma da kiyaye muhalli, shi ya sa tana ci gaba da kyautata tsarin neman bunkasuwa, lamarin da ya kasance babban dalilin da ya sa, ake samun ci gaba bisa fannoni daban daban cikin sauri a kasar Sin.

Haka kuma, an yi amanna cewa, kasar za ta ci gaba da cimma nasarori bisa fannoni daban daban a nan gaba, bisa jagoranci na JKS. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China