in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta tura sojoji zuwa yankin tafkin Chadi
2017-10-31 20:03:25 cri
Babban hafsan mayakan kasa na Najeriya laftana janar Tukur Buratai ya bayyana cewa, Najeriya ta tura dakaru zuwa yankin tafkin Chadi domin kakkabe gyauron mayakan kungiyar Boko Haram dake yankin.

Buratai wanda ya bayyana hakan ga taron manema labarai yau Talata, ya ce dakarun da aka tura za su gudanar da wannan aiki ne cikin hadin gwiwa a yankin tafkin Chadi da kewaye, domin gano da kuma kawar da ragowar gyauron mayakan na Boko Haran dake barna a yankunan dake kan iyakokin kasashen da ke makwabtaka da Najeriya. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China