in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha da Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar nukilya
2017-10-31 10:35:46 cri
Kasashen Rasha da Najeriya sun sanya hannu kan yarjejeniyar gina tashar nukiliya da nufin samar da makamashi da kuma cibiyar bincike a Najeriyar.

Cibiyar samar da makamashi ta kasar Rasha wato Rosatom ta sanar a ranar Litinin cewa, an cimma yarjejeniyar ne a lokacin taron ministocin kasashen duniya game da amfani da makamashin nukiliya marar illa wanda aka gudanar a Abu Dhabi, babban birnin hadaddiyar daular larabawa, inda aka nazarci matakan da za'a bi wajen amfani da kimiyyar makamashin nukilya don samar da zaman lafiya.

Anton Moskvin, mataimakin shugaban hukumar samar da makamashi ta Rusatom ya bayyana cewa, wannan wani babban aiki ne mai matukar muhimmanci, wanda zai kara karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu cikin dogon lokaci.

Mista Moskvin ya bayyana cikin sanarwar cewa, cigaban fasahar nukiliya zai baiwa Najeriya damar daukaka matsayinta na zama babbar jagora a nahiyar Afrika.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China