in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Koriya ta Kudu sun yi musanyar ra'ayi kan dangantakarsu
2017-10-31 13:42:26 cri
Rahotanni daga ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin na cewa, kwanan baya, mai taimakawa ministan harkokin wajen Sin Kong Xuanyou, da mataimakin ministan tsaro na kasar Koriya ta Kudu, Nam Gwan Pyo, suka yi musanyar ra'ayoyi, dangane da wasu muhimman batutuwa, ciki har da batun zirin Koriya.

Bangarorin biyu sun sake cimma matsaya daya kan wasu ka'idojin da za su bi, ciki har da kawar da dukkanin makaman nukiliya a zirin Koriya, da warware matsalar makaman nukiliya na Koriya ta Arewa cikin lumana.

Har wa yau, bangaren Koriya ta Kudu ya kara fahimtar matsayin gwamnatin kasar Sin kan batun girke na'urorin kakkabo makamai masu linzami sanfurin THAAD, inda ya tabbatar da cewa, girke wadannan na'urorin a Koriya ta Kudu ba ya da nufin kawo barazana ga wasu kasashe, wato ba zai yi illa ga harkokin tsaro na kasar Sin ba. Ita ma kasar Sin ta sake nanata kin amincewarta game da girke wadannan na'urorin THAAD a Koriya ta Kudu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China