in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kalubalanci Amurka da Koriya ta Kudu da su dakatar da kuma soke girke na'urorin THAAD nan take
2017-06-01 20:37:51 cri

Yau Alhamis ne Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana a nan Beijing cewa, girke na'urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin THAAD da kasar Amurka take yi a kasar Koriya ta Kudu, yana barazana ga harkokin tsaron kasar Sin, tare da lalata daidaito a yankin, kuma lamarin ba zai taimaka a kokarin da ake na kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya da kuma wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin ba. kasar Sin ba ta goyi bayan wannan mataki

Rahotanni na cewa, Amurka ta kai na'urorin kakkabo makamai masu linzami gami da nau'rorin harba makamai masu linzama guda 4 zuwa Koriya ta Kudu a asirce. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China