in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Koriya ta Kudu suna tuntubar juna yadda ya kamata
2017-01-06 20:40:45 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya ce har kullum kasar Sin na dora muhimmanci kan raya hulda a tsakaninta da kasar Koriya ta Kudu, tana kuma mu'amala da gwamnatin kasar, da ma sassa daban daban na kasar, yayin da a daya hannun ma'aikatun harkokin wajen kasashen 2 ke ci gaba da tuntubar juna yadda ya kamata.

An labarta cewa, kasar Sin na nuna adawarta da shirin jibge makamai, karkashin tsarin kandagarkin makamai masu linzami da ake kira THAAD a Koriya ta Kudu. Game da hakan ne ma a kwanan baya, kasar ta Sin ta tuntubi jam'iyyun 'yan hamayyar kasar a maimakon mahukuntan kasar, a wani mataki da gwamnatin Sin ta fara dauka na samun mafita. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China