in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zaben Kenya ta gabatar da sakamakon kidaya kuri'un zaben shugaban kasar da aka sake
2017-10-31 10:12:27 cri
Hukumar zabe da lura da harkokin kan iyakar kasar Kenya, ta gabatar da sakamakon kidaya kuri'un zaben shugaban kasar da aka sake a jiya ranar 30 ga wata cewa, inda ta bayyana dan takarar jam'iyyar Jubilee, kuma shugaban kasar na yanzu Uhuru Kenyatta a matsayin wanda ya lashe zaben na ranar 26 ga wannan wata. Bisa sakamakon, Kenyatta ya samu kuri'u da yawan su ya kai kashi 98.3 cikin dari.

Bayan da aka gabatar da sakamakon zaben, Kenyatta ya yi jawabi, inda ya nuna godiya ga masu jefa kuri'un a wannan karo, kana ya yi kira ga jama'a da su kiyaye zaman lafiya da tabbatar da hadin kai.

Bisa kididdigar da hukumar zaben kasar ta fitar, mutane miliyan 7 da dubu 600, cikin jimillar masu jefa kuri'u a zaben, wanda ya kunshi fiye da mutum miliyan 19 da dubu 600 da suka yi rajista ne suka jefa kuri'un su.

Ko da yake an gudanar da zaben a yawancin yankunan kasar, amma a sakamakon barazanar tsaro, ba a kada kuri'u a yankuna 25 ba a ranar 26 ga watan, wato adadin da ya kai kashi 8.6 cikin dari na adadin yankunan da suka yi zaben a karon farko.

Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Kenya suka bayar a wannan rana cewa, kawancen 'yan adawa na NASA, ya ki amincewa da sakamakon zaben da aka yi a ranar 26 ga wannan wata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China