in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zaben Kenya ta dage zabe a wasu yankunan dake fama da zanga-zanga
2017-10-27 11:07:50 cri

Hukumar zaben kasar Kenya, ta ce ta dage gudanar da zabe a wasu yankunan yammacin kasar 4 da ake zanga-zanga zuwa ranar Asabar.

Hukumar ta ce ta dakatar da zabe a yankunan Homa da Siaya da Migori da kuma Kisumu, inda 'yan adawa suka fi yawa, saboda tsaikon da zanga zanga da barazana kan jami'an zabe suka haifar.

Zanga-zangar adawa da zaben ya barke ne a yammacin kasar da ya kasance matattarar 'yan adawa da kuma yankin Kibera na Nairobi, a daidai lokacin da aka fara gudanar da sabon zaben shugaban kasar a jiya Alhamis.

Rikici ya barke tsakanin masu zanga-zanga da 'yan sanda, inda suka yi musayar wuta a yankunan, a lokacin da 'yan sanda ke sintiri yayin da aka fara zaben. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China