in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sake babban zabe a Kenya
2017-10-26 20:21:57 cri
A yau Alhamis, masu zabe a kasar Kenya sun sake fita rumfunan zabe da aka kafa a sassa daban daban na kasar, domin kada kuri'un su a zaben shugaban kasar da aka gudanar a sabon zagaye.

An yi rajistar masu zabe kusan miliyan 20 a duk fadin kasar. Da misalin karfe shida, agogon kasar, aka fara zaben, kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar ta ce, ana sa ran za a kawo karshen kada kuri'ar da misalin karfe biyar na yammacin ranar. Amma za a tsawaita lokacin a wasu rumfunan zabe da ba a bude su kan lokaci ba.

An ce, shugaban 'yan adawar kasar da ya yi kira da a kauracewa zaben, duk da cewa sunansa yana kan takardar zaben.

Kafofin watsa labarai na kasar sun bayyana cewa, domin zaben ya gudana yadda ya kamata, Kenya ta jibge 'yan sanda sama da dubu 13. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China