in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin wasu kasashe da na jam'iyyun siyasa na Afirka sun taya Xi Jinping murnar zama babban sakataren JKS
2017-10-27 11:12:02 cri
Shugabannin wasu kasashe da na jam'iyyun siyasa na Afirka suna ci gaba da aiko da sakwanni ko buga waya, inda suka taya Xi Jinping murnar zama babban sakataren kwamitin koli na jam'iyyar kwaminis ta Sin karo na 19

Shugaban Jamhuriyar Nijar, Mahamadou Yusuf ya bayyana a cikin sakonsa cewa, jam'iyyar kwaminis ta Sin gami da jama'ar kasar Sin sun goyi-bayan Xi Jinping don zama babban sakataren jam'iyyar ne, saboda namijin kokarin da ya yi a fannin raya kasa, da jagorantar kasar ta za ta kara samun ci gaba da wadata, abun da ya sa Sin ta samu yabo matuka daga fadin duniya.

A nasa sakon shugaban Jamhuiyar Mali, Ibrahim Boubacar Keita, cewa ya yi, Xi ya sake zama babban sakataren jam'iyyar kwaminis ta Sin, saboda dimbin nasarorin da kasar Sin ta samu a yayin da yake jagorancin jam'iyyar. Keita yayi imanin cewa, Xi Jinping zai ci gaba da dukufa kan aikin raya kasar Sin gami da kyautata zaman rayuwar al'ummar kasar a cikin sabon wa'adin aikinsa.

Shi kuma a nasa sakon, shugaban kasar Saliyio, kana jagoran jam'iyyar All People's Congress (APC) Ernest Bai Koroma, ya ce, a madadin gwamnati da jama'ar Saliyo, ya taya Xi Jinping murnar sake zama babban sakataren kwamitin koli na jam'iyyar kwaminis ta Sin. Koroma ya kuma nuna matukar godiyarsa ga Xi Jinping, saboda tallafi da taimakon da ya baiwa gwamnati gami da jama'ar kasar Saliyo.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China