in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta horas da jami'an tsaron Somaliya game da dokokin hakkin bil adama na kasa da kasa
2017-09-27 10:29:39 cri
MDD ta bayyana cewa ta fara gudanar da shirin bada horo na tsawon makonni biyu ga dakarun tsaron kasar Somaliya su 63, game da fahimtar hakkin dan adam da kuma dokokin kasa da kasa.

Ofishin samar da tallafi na MDD dake Somalia (UNSOM) ya sanar da cewa, mahalarta bitar za su samu kyakkyawar fahimta game da irin rawar da za su taka wajen gudanar da ayyukansu na kare rayuwar fararen hula, da mutane marasa galihu, da wadanda aka mayar da su saniyar ware musamman mata da kananan yara.

Taron bitar wanda ke gudana a Baidoa, dake kudu maso yammacin babban birnin kasar, ya samu halartar rundunar sojin kasar Somaliya SNA, da kuma dakarun 'yan sanda na musamman na kudu maso yammacin kasar Somaliya.

Ministar mata da kare hakkin bil adama ta jihar kudu maso yammacin kasar Somaliya Nadifa Armey Abdullahi, ta bayyana cewa taron bitar zai taimakawa jami'an tsaro wajen samun kyakkyawar fahimtar hakkin bil adama, kasancewa suna ta'ammali da bangarorin al'umma daban daban. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China