in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kira da a kara tura sojojin kiyaye zaman lafiya zuwa kasar Afirka ta Tsakiya
2017-10-28 13:51:48 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya ce ya kamata a kara tura sojojin kiyaye zaman lafiya zuwa kasar Afirka ta Tsakiya don tinkarar halin zaune-tsaye da kasar ke ciki a shekarun baya-bayan nan.

Antonio Guterres wanda ya kammala ziyarar kwanaki 4 da ya kai kasar ta Afirka ta Tsakiya, ya bayyana haka ne a jiya, a zauren majalisar dokokin kasar dake birnin Banji.

Sakatare Janar din ya kara da cewa, zai gabatar da shawarar kara yawan membobin tawagar kiyaye zaman lafiya ta MDD dake kasar ga kwamitin sulhu na Majalisar, don kara mata karfin sojoji.

Baya ga haka, Guterres ya bayyanawa membobin majalisar dokokin cewa, za a taimakawa kasar wajen kafa wata rundunar soji mai karfi sannu a hankali, wadda za ta maye gurbin sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD dake kasar.

A halin yanzu, yawan membobin tawagar kiyaye zaman lafiyar ya zarce dubu 12 da dari 5, inda Guterres ya bayyana cewa, ya kamata a kara yawansu da 900. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China