in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 8 sun mutu a sakamakon rikicin da ya barke a gabashin kasar Afirka ta Tsakiya
2017-08-31 13:33:27 cri
Hukumar kula da harkokin jin kai ta MDD ta fitar da sanarwa a kwanakin baya wadda ke cewa, mutane a kalla 8 sun mutu a sakamakon rikicin da ya barke a gabashin Afirka ta Tsakiya a kwanakin baya, kana wasu gidaje sun lalace a wasu kauyuka, baya ga mutane da dama da suka rasa gidajensu.

A shekarun baya baya nan, an sha samun tashe-tashen hankula a Afirka ta Tsakiya, gami da rikice-rikice a tsakanin kungiyoyin dakarun kasar, wadanda suka haddasa fararen hula da dama rasa gidajensu, an kuma kai wasu hare-hare kan masu aikin ceto da ma'aikatan kiyaye zaman lafiya a kasar.

Mataimakin babban sakataren MDD mai kula da harkokin jin kai Stephen O'Brien ya bayyana bayan da ya kai ziyara Afirka ta Tsakiyar a watan Yuli cewa, rikicin dake faruwa tsakanin kungiyoyin dakarun kasar ya rikide zuwa kisan kare dangi. Alkaluman MDD na nuna cewa, a watan Yuli kadai, mutane kimanin miliyan 2 da dubu 400 ne ke neman agaji a kasar, adadin da ya kai rabin adadin al'ummar kasar. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China