in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin Firaministan kasar Sin ya gana da sakataren harkokin cinikayya na Amurka
2017-10-28 13:51:46 cri

Mataimakin firaministan kasar Sin Wang Yang, ya gana a jiya Jumma'a ta wayar tarho da sakataren harkokin cinikayya na Amurka.

Jami'an biyu sun yi zuzzurfar tattaunawa kan shirye-shiryen sakamakon harkokin tattalin arziki da ake hasashen samu yayin ziyarar da Shugaban Amurka Donald Trump zai kawo kasar Sin, tare kuma da sauran wasu batutuwan dake da alaka da huldar cinikayya da tattalin arziki dake tsakanin Kasar Sin da Amurka.

Ana sa ran Shugaba Donald Trump zai kawo ziyara kasar Sin a watan gobe, a wani bangare na ziyarar da zai kai kasashe 5 na nahiyar Asiya da suka hada da Japan da Koriya ta Kudu da Vietnam da Philippines. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China