in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bada umarnin kama wasu mutane 834 da ake zargin 'yan ta'adda ne a Libya
2017-10-10 10:09:11 cri
Atoney Janar na Libya, ya bada umarnin kama wasu mutane 824 da ake zargin 'yan ta'adda ne a kasar.

Babban lauya mai shigar da kara na ofishin atoney janar na kasar Al Seddiq Al-Sour, ya ce an bada umarnin kama mutanen da ake zargi 824 ne karkashin tsarin bincike da shigar da kararraki kan ayyukan ta'addanci da kuma barazanar tsaro, yana mai cewa an bada sunayensu a shingayen bincike dake kan iyakokin kasar domin daukar matakin da ya dace.

Ya kara da cewa, ita ma hukumar 'yan sanda ta duniya INTERPOL ta bada umarnin kame wasu daga cikin mutanen da ake zargi.

Al Seddiq Al-Sour ya ce an tattara sunayen ne yayin da ake bincike tare da kame wasu 'yan ta'adda a birane daban-daban na kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China