Ayob Qasem ya bayyana cewa, 'yan cin rani sun nitse a tekun Zuwara, wanda keda tazarar kilomita 120 daga yammacin Tripoli babban birnin kasar Libyan, a lokacin da suke kokarin haurewa zuwa kasashen turai.
Jamai'an gudanarwa a tekun na Zuwara sun yi nasarar ceto mutane 7 ne da ransu a wani komi a wajen mai tazarar kilomita 20 daga tekun, inji Qasem.(Ahmad Fagam)