in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#JKS19#Hukumar kasar Sin ba za ta tattauna da ko wace jam'iyyar yankin Taiwan ba sai dai ta amince da ra'ayi bai daya da aka samu a shekarar 1992
2017-10-18 12:10:45 cri

Rahoton JKS ya nuna cewa, ka'idar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya tushen siyasa ne na dangantakar da ke tsakanin bangarori biyu na mashigin tekun Taiwan. Ra'ayin bai daya da aka samu a shekarar 1992 wanda ya amince da wannan ka'ida, wani muhimmin abu ne da ya tabbatar da bunkasar dangantaka yadda ya kamata. Muddin aka amince da wannan ra'ayi na bai daya, to bangarorin biyu za su iya tattaunawa da juna, kuma ko wace jam'iyya da kungiya da ke yankin Taiwan, ba za ta gamu da cikas ba yayin cudanya da babban yankin kasar Sin. Rahoton ya kuma jaddada cewa, babban yankin kasar Sin na da aniya da kuma karfi sosai wajen murkushe duk wani yunkurin neman kawo baraka ga kasar Sin. (Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China