in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya mika sakon jaje game da iftila'in zaftarewar laka da ya auku a Saliyo
2017-08-18 09:38:30 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sako ga takwaransa na Saliyo Ernest Bai Koroma, inda ya yi masa jaje game da iftila'in zaftarewar laka da mamakon ruwan sama ya haifar, al'amarin da ya janyo asarar rayuka da dukiya a kasar dake yammacin Afrika.

Cikin sakonsa, Xi Jinping a madadin gwamnati da al'ummar kasar Sin, ya jajantawa wadanda iftila'in ya rutsa da su tare da iyalansu.

Da sanyin safiyar Litinin da ta gabata ne gefen wani tsauni ya ruguje yayin da ake ruwan sama kamar da bakin kwarya, abun da ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 300 tare da raba wasu sama da 2,000 da muhallansu a wajen Freetown, babban birnin kasar Saliyo. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China