in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in MDD ya bukaci a dauki matakan dakile abubuwan dake haddasa karuwar talauci
2017-10-18 10:19:08 cri
Sakatare janar na MDD Antonio Guterres, ya buakci a dauki matakan shawo kan matsalolin dake haddasa karuwar talauci domin kawar da su daga doron kasa.

Da yake tsokaci game da muhimmancin dake tattare da ajandar dawwamamman ci gaban duniya nan da shekarar 2030, babban jami'in MDD ya bayyana cikin wani sakon bidiyo don bikin tunawa da ranar kawar da talauci ta duniya cewa, wannan ajanda wanda duniya baki daya ta amince da ita, za ta samar da wata irin duniya mai cike da zaman lafiya da kuma kyautata rayuwar al'ummar dake rayuwar a duniyar da kare martabar al'ummar duniya baki daya.

Mista Guterres, ya bukaci a dauki matakan da za su dakile karuwar talauci domin kawar da wannan matsala baki daya daga doron kasa, kana idan ana son magance wannan matsalar, dole ne a saurari ra'ayoyin mutanen dake fama da talaucin, kuma a gudanar da aikin tare da su muddin ana son kawo karshen matsalar daga doron kasa.

Sama da mutane miliyan 800 ne ke fama da talauci a fadin duniya, kuma mutanen suna ci gaba da rayuwa ne cikin matsanancin talauci, kana wasu mutanen masu yawa kuma suna fama da barazanar karuwar rashin aikin yi, da rashin tsaro, da rashin daidaito, da kuma matsalar da suke fuskanta sakamakon sauyin yanayi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China