in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin: Ya kamata a mayar da hankali kan kasashen dake tura sojoji a aikin wanzar da zaman lafiya na MDD
2017-10-06 17:29:02 cri

Mukaddashin shugaban zaunanniyar tawagar kasar Sin da ke MDD Wu Haitao ya bayyana jiya Alhamis, cewar kasashen dake aika sojoji da 'yan sanda su ne kashin bayan aikin wanzar da zaman lafiya na MDD, ya kamata a mayar da hanlali kan rawar da irin wadannan kasashe ke takawa

Wu ya kara da cewa, a cikin shekaru biyu da suka gabata, kasar Sin ta horar da masu wanzar da zaman lafiya fiye da 800 don MDD da kasashen da abin ya shafa, kuma ta aika da rukunin farko na jiragen sama masu saukar ungulu don taimaka wa MDD wajen gudanar da aikin wanzar da zaman lafiya a Afirka. Ban da wannan, kasar Sin na kokarin aiwatar da shirin samar wa kungiyar tarayyar Afirka AU taimako ta fuskar aikin soja da darajarsa ta kai dala miliyan 100, baya ga taimakawa kasashen dake tura sojoji musamman ma kasashen Afirka wajen kara karfinsu na samar da zaman lafiya, yayin da kasar Sin da MDD ke kokarin samar da asusun wanzar da zaman lafiya.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China