in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jagoran zaman MDD ya bukaci da a kara himma wajen dakile aukuwar tashe tashen hankula
2017-10-03 12:59:18 cri
Jagoran babban zaman mahawara na MDD Miroslav Lajcak, ya bukaci da a kara himma, wajen dakile aukuwar tashe tashen hankula a sassan duniya daban daban.

Mr. Lajcak wanda ya yi wannan kira a jiya Litinin, a wani bangare na bikin ranar kasa da kasa ta kaucewa tashe tashen hankula, ya ce ya kamata MDD ta kara azama, wajen kaucewa amfani da karfi a muhimman sassan ayyukanta 3, wadanda suka hada da wanzar da zaman lafiya da tsaro, da kare hakkokin bil Adama, da kuma na samar da ci gaba. Ya ce batun shiga tsakani, na daga matakai managarta na kaucewa amfani da karfi a ayyukan majalissar.

Kaza lika Mr. Lajcak ya ce hakan dabara ce ta sanya bangarorin da ba sa ga maciji da juna komawa teburin shawarwari.

Da ya tabo babban taron majalissar karo 72 da ya kammala a makon jiya, jami'in ya ce kiraye kiraye da kasashe mambobin majalissar, da hukumomi tare da kungiyoyin kasa da kasa suka gabatar, na kaucewa amfani da karfin tuwo wajen wanzar da zaman lafiya na da ma'anar gaske.

Mr. Lajcak ya ce yanzu haka MDD ta shiga wani mataki na gudanar da gyare gyare ga tsarin ayyukanta, don haka yake kira ga masu ruwa da tsaki a ayyukan nata, da su rungumi kudurin nan na samar da yanayin zaman lafiya a sassan duniya ba tare da murda kwanji ba.

Wani kudurin MDD na shekarar 2007 ne dai ya tanaji kebe ranar 2 ga ko wane watan Oktoba, a matsayin ranar kasa da kasa ta kaucewa amfani da karfin tuwo, ranar da ta yi daidai da ranar haihuwar jagoran juyin juya halin nan dan kasar Indiya Mahatma Gandhi, wanda ya jagoranci gwagwarmayar samun 'yancin kan kasar, tare da kafa akidar kaucewa amfani da karfin tuwo.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China