in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Iraki ya ba sojojin gwamnati umarnin shiga jihar Kirkuk
2017-10-16 13:04:08 cri
Da safiyar yau Litinin ne firaministan kasar Iraki, kuma kwamandan sojojin kasar Haider al-Abad ya ba sojojin gwammati umarnin shiga jihar Kirkuk wadda take fuskantar matsalar ikon mallaka.

Gidan telebijin na kasar ya ruwaito cewa, bisa umurnin firaministan, tuni aka jibge sojojin gwamnatin kasar, ciki har da sojojin yaki da ta'addanci da 'yan sanda da sauran jami'an tsaro a wasu yankunan dake jihar Kirkuk.

Babu kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin jihar Kirkuk da gwamnatin tsakiya ta kasar Iraki, kuma dakarun Kurdistan sun mallaki wasu yankuna, ciki har da jihar Kirkuk wadda ke fuskantar matsalar ikon mallaka, inda aka yi wa yankunan lakabi da "yankunan rikici".

Manazarta sun yi hasashen cewa, idan sojojin gwamnatin tsakiya na kasar suka shiga yankin ba tare da samun izni ba, zai iya haifar da rikici. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China