in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta yi gargadin dakatar da aiwatar da yarjejeniyar karin batutuwa ta hana yaduwar makaman nukiliya
2017-10-16 10:44:25 cri
Shugaban hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasar Iran Ali Akbar Salehi ya yi gargadin cewa, idan aka soke yarjejeniyar nukiliyar kasar a dukkan fannoni, kasar za ta dakatar da aiwatar da karin yarjejeniyar da aka cimma na hana yaduwar makaman nukiliya.

Kamfanin dillancin labaru na kasar Iran ya ruwaito Ali Akbar Salehi na bayyanawa 'yan jarida cewa, a matsayinta na kasar da ta sa hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya, Iran ta daddale yarjejeniyar kan karin wasu batutuwa don cimma burin hana yaduwar makaman, sai dai majalisar dokokin kasar ba ta kai ga zartar da ita ba, a don haka ya ce ba ta da wani amfani.

Ya ce idan aka soke yarjejeniyar nukiliya kasar, to babu bukatar ta ci gaba da aiwatar da waccan yarjejeniyar kan karin batutuwa.

Har ila yau, ya ce, idan Iran ta lura cewa, yarjejeniyar nukiliyar ba ta amfana mata, to za ta dawo da aikin tace sinadarin Uranium da kashi 20 cikin dari, a cewarsa kasar za ta dawo da aikin cikin kwanaki hudu.

Ali Salehi ya kuma zargi shugaban kasar Amurka Donald Trump da nuna kiyayya ga Iran da kin bincike kan sansanin sojan kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China