in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matakin Amurka na ficewa daga yarjejeniyar nukiliyar Iran ya haifar da damuwa a duniya
2017-10-14 17:07:41 cri
Sanarwar da shugaga Donald Trump na Amurka ya bayar game da janye kasarsa daga yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran da aka cimma, ta haifar da damuwa a ciki da wajen kasar.

Babban darektan hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya (IAEA) Yukiya Amano ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, Tehran tana baiwa hukumarsa hadin kai wajen aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma.

Matakin da Amurkar ta dauka bai yiwa kawayenta na yankin Turai da ma wadanda ke yankin tekun Atilantika dadi ba.

Jim kadan bayan sanarwar ce, sai kasashen Burtaniya da Faransa da Jamus suka fitar da wata sanarwar hadin gwiwa, inda suka bayyana cewa, su kam suna nan daram a kan wannan yarjejeniya, kuma ba sa tare da Trump a kan wannan mataki.

Ita ma ma'aikatar harkokin wajen kasar Rasha, ta bayyana cewa, babu wata kasa da za ta yiwa harkar diflomasiyar duniya barazana, kuma irin wannan mataki ba zai je ko'ina ba. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China