in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Iran: Fice daga yarjejeniyar nukiliya ta Iran zai kawo mugun tasiri ga Amurka
2017-10-12 10:50:49 cri
Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani ya bayyana a gun taron ministoci na kasar a ranar 11 ga wata cewa, idan shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi watsi da yarjejeniyar batun nukiliya ta kasar Iran, sai kamar ya sake yin kuskuren da Amurka ta taba yi a baya ne, zai iya kawo mugun tasiri ga kasar Amurka.

Shugaba Rouhani ya bayyana cewa, tabbatar da yarjejeniyar batun nukiliya ta kasar Iran yana da nasaba da mutuncin kasashen da suka sa hannu da kuma imanin kasa da kasa. A halin yanzu, sauran kasashen da suka sa hannu kan yarjejeniyar ba su amince kasar Amurka da ta janye daga yarjejeniyar ba, kasashe kalilan ne suka nuna goyon baya ga kudurin da Amurka ta yi.

Bayan da shugaba Trump ya hau kujerar shugaban kasar Amurka, ya nuna ra'ayi mai tsanani ga kasar Iran, kana ya ce Amurka za ta janye daga yarjejeniyar batun nukiliya ta Iran, amma kasar Iran ta jaddada cewa, ba za ta amince da sake yin shawarwari ba. Kafofin watsa labaru na kasa da kasa sun yi hasashe cewa, shugaba Trump zai sanar da sabbin manufofin da zai aiwatar kan kasar Iran, ciki har da kin amincewa da Iran din ta bi yarjejeniyar batun nukiliyata, kana zai mika rokon mayar da sakawa Iran takunkumi ga majalisar dokokin kasar Amurka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China