in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta bukaci kasashen duniya da su yi watsi da kungiyar IPOB
2017-10-14 11:40:58 cri
Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga abokan huldarta na kasa da kasa da su yi fatali da kungiyar nan dake fafutuwar neman 'yancin yankin Biafra (IPOB) kana su daina tallafa mata da kudade.

Ministan watsa labarai da al'adu na Najeriya Lai Mohammed shi ne ya yi wannan kiran cikin wani sharhi da ya rubuta mai take "Yaki da ayyukan ta'addanci a Najeriya" wanda aka wallafa ranar Alhamis a jaridar Washington Times ta kasar Amurka.

Ministan ya ce, Najeriya ba ta dade da yakar daya daga cikin kungiyoyin masu tayar da kayar baya a kasar ba, a don haka bai kamata a baiwa kungitar ta IPOB wata dama da za ta samu gindin zama ba. Ya ce ayyukan da kungiyar ke gudanarwa ne ya sa aka ayyana ta a matsayin ta ta'addanci. Inda take zama barazana ga mutanen da take wakilta, domin babu abin da kungiyar ta sanya a gaba illa batun neman ballewa.

Ministan ya jaddada cewa, gwamnati ba za ta sake yin kuskure ta bar wata kungiyar 'yan ta'adda ta kama wani yanki na kasar ba.

Idan ba a manta ba a ranar 20 ga watan Satumban wannan shekara ce, gwamnatin Najeriya ta soke kungiyar ta IPOB dake fafutukar neman 'yanci a kudu maso gabashin kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China