in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sama da yara 50,000 ne suka zama marayu sakamakon hare-haren kungiyar Boko Haram a Najeriya
2017-10-06 12:02:35 cri

Gwamnan jihar Borno dake yankin arewa maso gabashin Najeriya Kashim Shettima, ya bayyana cewa, kimanin yara 52,311 ne suka zama marayu a jihar ta Borno sakamakon hare-haren kungiyar Boko Haram a yankin arewa maso gabashin kasar.

Gwamnan wanda ya bayyana hakan ga manema labarai jiya Alhamis a birnin Maiduguri, fadar mulkin jihar Borno, ya ce hare-haren kungiyar sun kuma raba mata 54,911 da mazajensu. A don haka ya ce muddin ba a yi wa tubkar hanci ba, lamarin na iya haddasa karuwar matsalar jin kai a jihar da ma yankin arewa maso gabashin kasar baki daya.

Ya ce, hukumomin jihar sun gano ilmi a matsayin hanyar magance wannan kalubale. Yana mai cewa, gwamnati ta himmatu wajen zuba jari a bangaren ilmi kana ta bullo da wasu shirye-shiryen agaji tare da hadin gwiwar gwamnatin tarayyar Najeriya, MDD da sauran abokan hulda na kasa da kasa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China