in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya da MDD sun tattauna game da dawo da 'yan gudun hijirar kasar
2017-09-20 20:26:18 cri
A jiya Talata ne mataimakin firaministan kasar Libya dake samun goyon bayan MDD Ahmad Maiteeq ya tattauna da mataimakiyar shugaban tawagar majalisar MDD dake aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Maria do Valle Ribeiro game da yadda za a aiwatar da yarjejeniyar sasantawa da gwamnati ta amince da ita.

Ofishin yada labarai na gwamnatin Libya mai matsuguni a birnin Tripoli ya bayyana cewa, karkashin wannan yarjejeniyar dai, za a dawo da 'yan gudujn hijirar Tawergha zuwa gida.

Jami'ar MDDr tana ganin nasarar sasantawar a matsayin wata dama ta samar da wani ginshi ga al'ummomin tare da kawo karshen matsalar da 'yan gudun hijirar ke fuskanta.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China