in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD da AU sun fitar da rahoto game da yadda za a gudanar da ayyukan jin kai a Somaliya
2017-09-10 12:05:16 cri
Tawagar MDD dake aikin wanzar da zaman lafiya a Somaliya (AMISON) da kungiyar tarayyar Afirka (AU) sun kaddamar da wani rahoton cikin hadin gwiwa kan irin nasarorin da aka cimma a ayyukan jin kai a kasar Somliya cikin shekaru uku da suka gabata da kuma yadda za a gudanar ayyukan jin kai nan gaba a cikin kasar.

Da yake karin haske kan hakan wakilin mataimakin musamman na shugaban hukumar zartarwar kungiyar tarayyar Afirka mai kula da Somaliya Simon Mulongo ya ce, dangantaka tsakanin AMISON da hukomomin agaji ta taimaka matuka wajen inganta tsarin samar da kayayyakin agajin ga al'ummomin da ke matukar bukata.

Mulongo ya ce sun ji dadin yadda sojoji da hukumomin bayar da agaji ke yin mu'amala, kuma hakan ya taimaka wajen inganta rayuwar al'ummomin dake matukar bukatar kayan agaji a kasar ta Somaliya.

A don haka ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su kara yin cudanya tsakanin sojoji da hukumomin bayar da agaji, don tabbatar da cewa, kayayyakin agaji su kai ga yankuna masu wahalar shiga. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China