in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba al-Bashir na Sudan ya goyi bayan shirin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudu
2017-09-29 10:37:28 cri
Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir, ya jaddada goyon bayan kasarsa na daukar dukkan matakan da za su tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a makwabciyar kasar Sudan ta kudu.

Da yake jawabi a taron kwamitin kwararru da wanzar da tsaro na kasashen Afrika (CISSA), karo na 14 a birnin Khartoum, al-Bashir ya ce Sudan tana aiki tukuru karkashin wasu managartan tsare tsare da Afrika ta bullo da su don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Sudan ta kudun.

Ya kuma nanata aniyar kasar Sudan na samar da kayayyakin tallafi ga mutanen da rikicin ya shafa a sabuwar yantacciyar kasar.

Shugaba al-Bashir ya ce, a shirye kasarsa take ta samar da tallafin jin kai ga jama'ar Sudan ta kudu kuma za su bude kofa domin ba da damar shigar da kayayyakin tallafi ga al'ummar kasar Sudan ta kudun. Kana ya kara da cewa, sun bude kofa ga 'yan gudun hijjirar Sudan ta kudun wadanda ke neman mafaka a kasar don ba su tsaro ga lafiyarsu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China