in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Kenya ya soki hukuncin babbar kotun kasar na soke zaben shugaban kasar
2017-09-22 09:07:02 cri
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta, ya bayyana hukuncin da kotun kolin kasar ta zartar na soke zaben shugaban kasar da aka gudanar na ranar 8 ga watan Augusta da cewa rashin adalci ne, kuma a cewarsa ya zama tilas kotun kolin kasar ta samar da karin hujjojin da suka sanya ta daukar wannan mataki.

Mista Kenyatta ya shedawa 'yan jaridu a Nairobi cewa, bai ga dalilin da zai sa sa kotun daukar wannan mataki na soke zaben da miliyoyin al'ummar Kenya suka amince da aiwatar da shi ba tare da wasu kwararan hujjoji ba.

Ita dai kotun kolin kasar dake zamanta a birnin Nairobi ta amince da soke sakamakon zaben wanda ya sake baiwa shugaba Kenyatta nasara da kashi 54 cikin 100 a kan abokin hamayyarsa Raila Odinga, wanda ya samu kashi 44 bisa 100 na yawan kuri'u a zaben da aka kada a watan jiya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China