in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kara zurfafa gyare-gyare don inganta yanayin kasuwanci
2017-09-29 09:29:30 cri
A jiya Alhamis ne majalisar gudanarwar kasar Sin ta yanke shawarar kara zurfafa yin gyare-gyare da nufin kawar da duk wani shinge dake yiwa yanayin harkokoin kasuwancin kasar tarnaki.

Wata sanarwar da majalisar ta fitar na nuna cewa, shirin yin gyare-gyaren da aka gwada a sabon yankin Pudong na birnin Shanghai, ya banbanta takardar iznin tafiyar da harkokin kasuwanci da lasisin yin kasuwanci, sannan ya takaita bayar da sabbin takardun iznin tafiyar da harkokin kasuwanci.

Sanarwar ta kara da cewa, yanzu haka shiyoyin cinikayya marasa shinge guda 10 dake sassa daban-daban na kasar, ciki har da wadanda ke garuruwan Tianjin, da Chongqing da lardunan Liaoning da Zhejiang za su fara aiwatar da shirin yin gyare-gyaren. Ana fatan shirin yin gyare-gyaren zai mayar da hankali wajen kawar da duk wasu shingaye game da samun iznin tafiyar da harkokin kasuwanci, amma kuma zai kara sanya ido da yin musayar bayanai.

A cikin shekaru biyar din da suka gabata, gwamnatin kasar Sin ta samarwa kamfanonin gida da na wajen yanayin kasuwancin da ya dace, ta hanyar samun takardun iznin tafiyar da harkokin kasuwanci cikin sauki, da rage biyan kudaden rajista da ayyukan hidima na zamani, a wani mataki na sakarwa kasuwa mara. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China