in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kama wasu jami'an gwamnatin jihar Ekitin Nijeriya bisa karkatar da kudaden tallafi
2017-09-29 09:03:00 cri
Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arziki tu'annuti ta Najeriya wato EFCC, ta tabbatar da kama manyan jami'ai 2 na gwamnatin jihar Ekiti, bisa zarginsu da karkatar da kudaden tallafi da gwamnatin tarayyar kasar ta ba jihohi.

Kakakin hukumar Wilson Uwajaren, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a jiya cewa, an kama jami'an ne bayan sun ki amsa gayyatar da hukumar ta yi musu a baya don amsa tambayoyi game da bincike da ake na karkatar da kudaden tallafi da gwamnatin Ayodele Fayose ta yi.

Wilson Uwajaren, ya ce jami'an da aka kama sun hada da kwamishinan kudi da babban akantan jihar.

Kamen ya zo ne a ranar da gwamna Ayodele Fayose na jihar, ya bayyana kudurinsa na tsayawa takarar shugaban kasar a zaben 2019 a hukumance. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China