in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta raba abinci ga iyalan 'yan gudun hijira a arewa maso gabashin kasar
2017-09-21 09:04:50 cri
A ranar Laraba gwamnatin Najeriya ta fara aikin rabon kayan abinci ga iyalai sama da dubu 40 a yankuna 7 da aka kwatosu daga hannun 'yan ta'adda na Boko Haram a jahar Adamawa dake arewa maso gabashin kasar.

Babban daraktan hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA Mustapha Maihaja, ya bayyana a garin Gombi cewa, wannan na daya daga cikin yunkurin gwamnatin kasar na bada tallafin abinci ga al'ummomin da rikicin Boko Haram ya shafa.

Maihaja ya ce, manufar bada tallafin shine, domin rage radadin ga jama'ar dake rayuwa a sansanin 'yan gudun hijirar, ya ce a wannan karo za'a bada tallafin ne ga iyalai sama da dubu 40, daga yankunan 7 wadanda rikicin ya daidaita a jahar.

Kayan da aka raba sun hada da buhhunan waken soya, gero, masara, flour, da kuma buhhunan semovita biyu dana masavita wanda aka yi kiyasin zasu iya amfani da kayan har tsawon wata guda.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China